CANAL+ INTERNATIONAL ya cimma yarjejeniyarta da tashar nishadantarwa da tsarin rayuwa a Najeriya, wato AREWA24.
Tashar wadda aka bude a shekarar 2014 don haskakawa tare da fito da al’adun Hausawa, AREWA24 na isa ga masu kallo da ke magana da harshen Hausa sama da milyan 80 a yammacin Afirka.
Tashar AREWA24 na gabatar da shirye-shirye masu nishadantarwa da tsarin rayuwa da dama, iri daban-daban, Kama daga shirye-shiryen Gari Ya Waye da na Mata da Matasa da shiryeshiryen Hip Hop, da Fina-finan Kannywood da shirin “Kundin Kannywood” da Girke-Girke da kuma Shirn al’adu da shirye-shirye na musamman.
Haka kuma shirye-shiryen talabijin na tashar AREWA24 sun hada da shirye-shiryen kiwon lafiya, da shirin yara da kada-kaden gargajiya da kuma wasannin kwaikwayo daban-daban na kasashen Indiya da Turkiyya masu dogon zango, wadanda duk aka fassarasu cikin harshen Hausa. Tashar nishadantarwa a Najeriya, AREWA24 na nan a kan na’urar tauraron dan adam ta Canal+ kan tasha mai lamba 285, wadda zata fara daga yau. Don haka ne, wannan sanarwa ke kaddamar da bude sabon rukunin tashohin talabijin a kasar Nijar.
Kamfanin CANAL+INTERNATIONAL yana kokarin ganin ya kara matsowa kusa da abokan huldarsa na Najeriya, domin fitar da hanyar biya musu bukatunsu. “Muna farin ciki da muka samun damar fadada shirye-shirye masu inganci da muke samarwa. Tashar AREWA24 tasha ce da ta ke samar da shirye shirye masu inganci tun daga shekarar 2014.
A halin yanzu CANAL+INTERNATIONAL ta iso kasar Nijar kuma muna fata mu bawa masu basira a kasar damar kaiwa ga dukkanin kasashen dake magana da harshen Faransanci a nahiyar Afirka. Manufarmu ita ce tallata nasarorin da Najeriya ta samu da kuma kulla wata alaka tsakanin bangarori daban-daban na nahiyar Afirka.” A cewar Cheikh Sarr, Babban Jami’in Canal + ta kasar Niger. “Mun yi farin cikin samun hadin guiwa da CANAL + INTERNATIONAL wajen nuna shirye-shirye masu inganci da harshen Hausa ga abokan huldarsu. Muna da tabbacin cewa shirye-sjiryenmu za su zaburar tare da nishadantar da sabbin masu kallonmu a kan CANAL + a kasar Nijar kamar yadda suke yi a tsawon shekaru biyar da suka wuce a Najeriya.” A cewar Celestine Umeibe, Shugaban sashen tallace-tallace na tashar AREWA24.
Game da AREWA24 : Za a iya sauke shirye-shiryen tashar AREWA24 a kowanne mako a kan youtube.com/AREWA24channel. Ku kasance da masu kallon tashar AREWA24 da ke k kafafen sada zumunta a kan: AREWA24.com, da https://facebook.com/AREWA24, da Instagram.com/AREWA24channel, da kuma twitter.com/AREWA24channel.
You Might also like
-
AREWA24 Na Cigaba Da Bunkasa Zuwa Ga Masu Magana Da Harshen Hausa Da Ke Ko Ina A Fadin Duniya
Tashar AREWA24, tasha ta Hausa da ke kan gaba a fagen nishadi da tsarin rayuwa a Najeriya da kuma yanmacin Afirka na sanar da kaddamar da “AREWA24 ON DEMAND,” wata sabuwar manhaja ta nuna shirye-shiryenta da ake kira subscription video-on-demand (“SVOD”) da “Over-the-Top” (OTT) a turance. A yanzu dukkanin masu magana da harshen Hausa da Iyalansu dake zaune a ko ina a fadin duniya, za su samu damar more kallon shirye-shiryen daban-daban da suka lashe lambar yabo, wadanda al’ummar Najeriya da na yammacin nahiyar afirka ke jin dadin kallonsu yau da kullum a kan tashar AREWA24 da ke nuna shirye-shiryenta a tsawon sa’o’i 24 a ranakun mako.
Shugaban tashar AREWA24, Jacob Arback, ya bayyana wannan sabuwar manhaja da cewa, wata hanya ce ta fadada hanyoyin yada shirye-shiryensu domin kaiwa ga dukkannin masu magana da harshen Hausa da ke fadin duniya. Ya ce “Sanya masu kallo su ji kamar suna gida da kuma jin suna alfahari da al’adunsu na gargajiya shi ne babban makasudin samar da wannan sabuwar manhaja ta AREWA24 ON DEMAND da ma tashar AREWA24 baki daya. A yanzu, masu kallonmu za su iya more kallon shirye-shieryen da suka yi fice, wadanda ke da alaka da garuruwansu, suke kuma nishadantar da iyali da masu magana da harshen Hausa a ko ina su, ta amfani da wannan sabuwar manhaja. Musamman ma yadda muke nuna al’adu na alfahari da kuma sanya Iyalan Hausawa da suke kasasen waje su ji kamar suna gida Najeriya ko kasashen Yammacin nahiyar Afirka.”
Arback ya kara da cewa, “za a kaddamar da manhajar AREWA24 ON DEMAND da dinbun shirye-shirye na musamman. “Muna shirya shirye-shirye da dama da suka shafi abubuwa daban-daban da salo daban-daban a kowacce rana a dakunan shirye-shiryenmu da ke garin Kano a Najeriya, wadanda suka hada da shararrun wasannin kwaikwayonmu masu dogon zango, wato “Kwana 90” da kuma “Dadin Kowa.” Haka kuma, muna fassara shirye-shiryen sassan fadin duniya da na yankin nahiyar Afirka da dama zuwa harshen Hausa dakunan daukar shirye-shiryenmu guda uku da muke da su, wadanda dukkaninsu za su kasance a kan wannan sabuwar manhaja.”
Sabuwar manhajar AREWA24 ON DEMAND SVOD za ta bada damar samun dukkanin shirye-shiryen tashar AREWA24 da kuma taskar ajiye shirye-shirye na harshen Hausa, wadda ita ce taskar shirye-shirye na harshen Hausa mafi girma a duniya. Baya ga wasannin kwaikwayo masu dogon zango da tashar ke shiryawa, sabuwar manhajar ta AREWA24 ON DEMAND za ta dinga kunsar sabbin shirye-shirye a kowacce rana, da suka hada da sabbin wasannin kwaikwayo na masana’antar Kannywood, da kuma shirye-shiryen Hausa Hip Hop, da na girke-girke, da shirye-shiryen da tashar ke kawo a kullum wato Gari ya waye, da shirye-shiryen wasanni, da na al’adu da shirin Bayan fagen fina-finan Kannywood, da shirye-shiryen mata da matasa da kuma yara, da ma wasu da dama. Manhajar AREWA24 ON DEMAND tana karkashin gudanarwar gudanar fasahar kanfanonin Vimeo’s state-of-the-art SVOD da kuma OTT technologies. Kamfanin Vimeo ne ke samar da dabaru masu inganci domin masu gudanar da ayyukansu ta yanar gizo su bawa abokan huldarsu damar kulla alaka da su a dukkanin manyan manhajoji da kuma na’urorin amfani da yanar gizo.
“Muna alfahari da damar da kamfanin fasahar Vimeo’s best-in-class OTT technology ya bamu, na kaiwa ga abokan hulda ba tare da wata sarkakiya ba, da kuma bada ingantacen yanayi ga tashar AREWA24 da kuma masoyanta,“a ta bakin Kathleen Barrett, SVP, Enterprise, na kamfanin fasahar Vimeo. “A yanzu masu kallo za su iya amfani da kuma morewa kallon sabuwar manhajar kallon shirye-shiryen harshen Hausa ta farko a manhajar da ake kira SVOD service a turance.”
Domin amfani da sabuwar manhajar AREWA24 ON DEMAND wato SVOD service, sai ku ziyarci adreshin yanar gizo http://tv.arewa24.com ko kuma ku sauke manhajar a kan wayoyinku daga kafofin IOS App Store, da Google Play, da Apple TV, da Roku Channel Store da kuma Amazon Fire TV.
GAME DA MANHAJAR AREWA24 ON DEMAND: Manhajar AREWA24 ON DEMAND, wani bangare ne na kamfanin Network AREWA24, Ltd, manhaja ce kallon dukkanin shirye-shiryen harshen Hausa da ake kira all-Hausa language global streaming da kuma OTT service a turance, da nufin yada al’adu na alfahari ga masu magana da harshen Hausa a fadin duniya. An kaddamar da wannan manhaja da kimanin sama da shirye-shirye 2,000 da suka shafi abubuwa daban-daban da salo daban-daban da suke da farin jini a Najeriya da kuma Yammacin nahiyar Afirka, wadanda suka hada da wasannin kwaikwayo masu dogon zango da tashar ke shiryawa, da sabbin wasannin kwaikwayo na masana’antar Kannywood, da hirarraki da shirye-shiryen mata da na Hip Hop da na matasa da kuma yara da shirin girke-girke, da na al’adu da ma wasu da dama.
GAME DA TASHAR AREWA24: Tahsar AREWA24 da shirye-shiryenta, An kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma
wasanni. A yau, tashar AREWA24 ta kai ga mutane milyan 38 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma yammacin nahiyar Afirka a kan tauraron dan dan’adam na Eutelsat da ake kallo kyauta, da kuma kan tauraron dan adam na StarTimes da ake biya (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ake biya, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101), da kuma tauraron dan adam na Canal+ payTV service (tasha mai lamba #285) a Jamhuriyar Niger, da Chad da kuma Cameroun. AREWA24 na amfana da masu kallo da ke kasancewa da dukkanin shafukanta na AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, Instagram.com/AREWA24channel, and twitter.com/AREWA24channel.
Domin karin bayani sai ku tuntubi: info@arewa24.com
Post Views: 7,788 -
Ina ma ‘KWANA CASA’IN’ na AREWA24 ya zama abin koyi
Fim din Kwana Casa’in, wato shirin Hausa dirama ne da a ke nunawa a tashar talabijin ta AREWA24, inda zubi da tsarin labarin ya sha bamban da finafinan da mu ka saba kallo, wanda ba su wuce tunanin yaro karami ba.
Labarin ya na magana ne a kan siyasar kasar nan da irin abubuwan da ke faruwa a jami’o’inmu da ma rayuwa ga bakidaya.
Tuntuni ya kamata a rika zakulo irin wadannan matsaloli, saboda su ne damuwarmu, amma sai finafinan da a ke kira na Hausa su ka duge ga rawa da waka da gasar nuna jiki da matsattsun wanduna.
A ciikin Kwana Casa’in, tsarin hoto kansa na daban ne, domin ya sha bamban da irin tsarin hoton da mu ka saba gani, saboda an yi amfani da na’urar daukar hoto mai matukar inganci ta yadda mai kallo zai ga kamar a gabansa abubuwan ke faruwa.Wuraren da a ka yi amfani da su irinsu asibitoci, ofisoshi, gidaje, makarantu ko gidan rediyo, nan ma abin jinjinawa ne, domin kuwa an yi amfani da wuraren da su ka dace ta yadda duk wanda ba dan kasa ba, idan ya kalla, zai ga tsantsar kama da gaskiya a cikin labarin, wanda hakan ma iyawa ce. Idan na nutsu Ina kallon Kwana Casa’in sai na ji tamkar gaske ne. Yadda masu mulki ke rayuwa da rayuwar talaka a wannan zamani da yadda a ke amfani da talaka, domin kama madafun iko duk an bayyanar da shi. Ina da yakinin kafin labarin ya kare mutane da dama za su dauki darasin rayuwa. Lokacin da na ga hotunan wasu jaruman Kannywood a cikin Kwana Casa’in kafin na fara kallon fim din, sai da na ji jiki na ya yi sanyi, saboda Ina tsoron kar su bata dirimar ta yadda za mu rika kallon ta kamar shirme, amma abin da ya burge ni shi ne yadda su ka shiga su ka bata a cikin shirin ba tare da kawo mishkila ko mayar da abin wasan yara ba. Hakan ya nuna ma ni kenan da za su sami labari mai inganci da kayan aiki, sannan su sako masu ilimin a cikin nasu shirye-shiryen, kila su ma za su samu su mike a Kannywood din kenan. Yadda jaruman su ka nuna dagiya da tsantsar kwarewa sosai, ya yi kyau matuka ta yadda ko wadanda su ka saba kallon finafinan kasashen ketare za su jinjina masu domin kasashen da su ka cigaba su na shirya dirama mai dogon zango ko finafinai kan matsalar da su ke fuska a kasar fiye da shirme irin wanda a ke yi a finafinan da mu ka saba gani. Da alama dai Kwana Casa’in shi ne labarin da ya ke kokarin taushe shirin dadin Kowa na Arewa 24 din dai, domin kamar yadda a ka kasa samun wani shirin dirama da zai yi karo da Dadin Kowa daga masana’antar Kannywood, watakila AREWA24 din ce dai kadai za ta iya yin karo shi da wannan sabon shiri tsararre na Kwana Casa’in. Tsawon lokacin da na dauka Ina kallon shirin Hausa na Kannywood lallai na gano wa Kannywood makarantar da za su kara ilmi. Sannu a hankali AREWA24 za ta maye gurbin shirin Hausa dirima, saboda su ne su ke tattauna abinda ya dame mu a kasa, ba rawa da juyi gaban allunan talabijin ba. Fadila H Aliyu Kurfi marubuciya ce mai sharhi kan al’amuran yau da kullum kuma ’yar gwagwarmaya.
Za a iya samun ta a imel: fadilakurfi@gmail.com ,
Facebook: Fadila H Aliyu Kurfi.
Read More at: https://hausa.leadership.ng/2019/04/18/ina-ma-kwana-casain-na-arewa-24-yazama-abin-koyi/Post Views: 8,021 -
AREWA24 Tana murnar cika shekaru 7 da kuma gagarumin sabbin shirye shirye da babu kamar su
28 ga watan Yuni, 2021 – Tashar AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba a fagen shirye-shirye na harshen Hausa masu nishadantarwa da tsarin rayuwa, kuma take da dakin daukar shirye-shirye a Najeriya da ke Yammacin Nahiyar Afirka, tana bukin cika shekaru bakwai da kafuwa, ta hanyar kawowa masu kallonta babban jadawalin sabbin shirye-shirye na harshen Hausa da ba a taba irinsa ba a tarihin tashar. Sabon jadawalin shirye-shiryen na tashar AREWA24 zai fara aiki ne a watan Yuli, kunshe da sabbin wasannin kwaikwayon tashar, da sabon shirin tattaunawa na mata, da sabbin shirye-shiryen yara don “Ilimantarwa da nishadantarwa” masu dogon zango, da sabbin shirye-shiryen wasan kwallon kafa, tare da sauran shahararrun wasannin kwaikwayon tashar AREWA24 da kuma sauran shirye-shiryen da take gabatarwa. Da yawa daga cikin wadannan shirye-shirye za kuma su kasance a kan manhajar AREWA24 On Demand nan take, manhajar tashar da ke bawa iyalai masu Magana da harshen Hausa da ke fadin duniya damar kallon shirye-shiryen Arewacin Najeriya masu nishadantarwa, da al’adu da kuma tsarin rayuwa. A halin yanzu ana ci gaba da daukar sabbin zangon shahararrun wasannin kwaikwayo masu dogon zango na tashar, wato Kwana Casa’in da Dadin Kowa, kuma za a fara nuna su a watan Oktoba.
Sabbin wasannin kwaikwayo na Hausa guda uku ne ke kan gaba a cikin sabon jadawalin shirye-shiryen AREWA24: Buka Africana, wani wasan barkwanci da aka shirya a wani gidan cin abinci da ke yankin Arewa ta tsakiya, ko “Buka.” Labarina-zango na-3, sabon zangon daya daga cikin shahararrun wasannin kwaikwayo masu dogon zango na Arewacin Najeriya da kuma Sirrin Boye, wani sabon wasan kwaikwayo da ya kunshi rudani da muggan laifuka. Haka kuma a watan Yuli, tashar AREWA24 za ta fara nuna wani gagarumin sabon shiri tattaunawa na mata, mai suna “Mata A Yau” (Today’s Woman), wanda ya kunshi masu gabatarwa mutum hudu da suka zo daga bangarori daban-daban na rayuwa, kuma masu shekaru daban-daban, da za su tattauna mahimman batutuwan da mata ke fuskanta a halin yanzu a Arewacin Najeriya.
Shugaban Tashar AREWA24, Jacob Arback, yayin da yake bayani game da cigaban da kamfanin ya samu tsawon shekaru bakwai, ya yabawa hukumar gudanar da kuma ma’aikatan kamfanin bisa gagarumin kwazon da suke nunawa a fagen talabijin, da kafafen yada labarai da kuma fasahar kirkira a Arewacin Najeriya. “Mutane da dama ba su fahimci cewa akwai mutane masu magana da harshen hausa sama da milyan 80 a Arewacin Najeriya da kuma yankin Sahel ba, kuma yankin na cike da matasa masu basira a ko’ina. Arback ya kara da cewa, “Sai dai, abin da na fi alfahari da shi, shi ne yadda hukumar gudanarwa da ma’aikatanmu suka tattaru daga bangarori na rayuwa daban-daban, da addinai, da kabilu, da kuma yankunan Najeriya daban-daban suka kasance ma’aikata a Jahar Kano a Najeriya, domin shirya kayatattun shirye-shiryen da ke fitowa daga nahiyar Afirka a yau.”
Tashar AREWA24 tana kuma fadada shirye-shiryenta na yara masu Ilimantarwa da kuma nishadantarwa a watan Yuli, A karon farko, an fassara shirin “Sesame Street Friends,” da ya lashe lambobin yabo da dama zuwa harshen Hausa, da dukkanin ‘yan wasan shirin da kuke so, da wasannin barkwanci, da zane mai motsi da kuma wasannin ‘yartsana. Haka kuma shirin Super Sema zai zo a tashar AREWA24 da harshen hausa, wanda shi ne shirin zane mai motsi na jaruman Afirka na farko mai dogon zango da aka shirya shi game da wata matashiyar yarinya da ta ke yin wani aiki na musamman don kare kauyensu da ke Afirka daga wani Azzalumi mara Imani da sojojinsa na butum-butumi masu naci. Jarumar da ta lashe lambar yabo ta Oscar, Lupita Nyong’o, tana daga cikin wadanda aka yi amfani da muryoyinsu a shirin na Super Sema mai dogon zango sannan kuma abokiyar hulda ce ga kamfanin kasar Kenya, Kukua da ya shirya shirin Super Sema. Domin faratawa ‘yan Najeria magoya bayan wasan kwallon kafa, Tashar AREWA24, a jadawalin shirye-shiryenta na watan Yuli, za ta fara nuna wasu sabbin shirye-shiryen wasanin kwallon kafa masu dogon zango, wato “Homage, da “Perfection.”
GAME DA TASHAR AREWA24: An kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen Hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, tashar AREWA24 tana kaiwa ga mutane sama da milyan 40 a Najeriya da kuma yammacin Afirka ta tauraron dan dan’adam na Eutelsat na kyauta, da da kafar tauraron dan adan na StarTimes da ake biya (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ake biya, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101), da kafar tauararon dan’adan ada ake biya ta TSTV (Tasha mail amba 361) da kuma ta Canal+ da ake biya (tasha mai lamba #285) a kasashen Nijar, Chadi da kuma Kamaru. Tashar AREWA24 na amfana da masu kasancewa da ita a dukkanin shafukanta na sada a kan adreshin AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, da kuma Instagram.com/AREWA24channel.
Domin yin rijista da tsarin kallo a ko’ina a duniya, wato AREWA24 ON DEMAND, sai ku ziyarci http://tv.arewa24.com ko kuma ku sauke manhajar daga IOS App Store, ko Google Play, ko Apple TV, ko Roku Channel Store da kuma Amazon Fire TV.
Domin Karin bayani sai ku tuntubemu a wannan adreshi: info@arewa24.com
Post Views: 6,130