CANAL+ INTERNATIONAL ya cimma yarjejeniyarta da tashar nishadantarwa da tsarin rayuwa a Najeriya, wato AREWA24.
Tashar wadda aka bude a shekarar 2014 don haskakawa tare da fito da al’adun Hausawa, AREWA24 na isa ga masu kallo da ke magana da harshen Hausa sama da milyan 80 a yammacin Afirka.
Tashar AREWA24 na gabatar da shirye-shirye masu nishadantarwa da tsarin rayuwa da dama, iri daban-daban, Kama daga shirye-shiryen Gari Ya Waye da na Mata da Matasa da shiryeshiryen Hip Hop, da Fina-finan Kannywood da shirin “Kundin Kannywood” da Girke-Girke da kuma Shirn al’adu da shirye-shirye na musamman.
Haka kuma shirye-shiryen talabijin na tashar AREWA24 sun hada da shirye-shiryen kiwon lafiya, da shirin yara da kada-kaden gargajiya da kuma wasannin kwaikwayo daban-daban na kasashen Indiya da Turkiyya masu dogon zango, wadanda duk aka fassarasu cikin harshen Hausa. Tashar nishadantarwa a Najeriya, AREWA24 na nan a kan na’urar tauraron dan adam ta Canal+ kan tasha mai lamba 285, wadda zata fara daga yau. Don haka ne, wannan sanarwa ke kaddamar da bude sabon rukunin tashohin talabijin a kasar Nijar.
Kamfanin CANAL+INTERNATIONAL yana kokarin ganin ya kara matsowa kusa da abokan huldarsa na Najeriya, domin fitar da hanyar biya musu bukatunsu. “Muna farin ciki da muka samun damar fadada shirye-shirye masu inganci da muke samarwa. Tashar AREWA24 tasha ce da ta ke samar da shirye shirye masu inganci tun daga shekarar 2014.
A halin yanzu CANAL+INTERNATIONAL ta iso kasar Nijar kuma muna fata mu bawa masu basira a kasar damar kaiwa ga dukkanin kasashen dake magana da harshen Faransanci a nahiyar Afirka. Manufarmu ita ce tallata nasarorin da Najeriya ta samu da kuma kulla wata alaka tsakanin bangarori daban-daban na nahiyar Afirka.” A cewar Cheikh Sarr, Babban Jami’in Canal + ta kasar Niger. “Mun yi farin cikin samun hadin guiwa da CANAL + INTERNATIONAL wajen nuna shirye-shirye masu inganci da harshen Hausa ga abokan huldarsu. Muna da tabbacin cewa shirye-sjiryenmu za su zaburar tare da nishadantar da sabbin masu kallonmu a kan CANAL + a kasar Nijar kamar yadda suke yi a tsawon shekaru biyar da suka wuce a Najeriya.” A cewar Celestine Umeibe, Shugaban sashen tallace-tallace na tashar AREWA24.
Game da AREWA24 : Za a iya sauke shirye-shiryen tashar AREWA24 a kowanne mako a kan youtube.com/AREWA24channel. Ku kasance da masu kallon tashar AREWA24 da ke k kafafen sada zumunta a kan: AREWA24.com, da https://facebook.com/AREWA24, da Instagram.com/AREWA24channel, da kuma twitter.com/AREWA24channel.
You Might also like
-
AREWA24 ta Kaddamar da shirinta na “Watan Gangamin Mayar da Hankali Kan Lafiyar Kwakwalwa” A Daukacin Watan Yuli
AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba wajen gabatar da shirye-shirye masu nishadantar da iyali da tsari rayuwa cikin harshen Hausa, wadda ke da ofishinta na samar da shirye-shirye a Najeriya da kuma yammacin Afirka, tana sanar da kaddamar da wani shirin wayar da kai na watan mayar da hankali kan kula da lafiyar kwakwalwa.
A cikin daukacin watan yuni, tashar AREWA24 za ta sadaukar da manyan bangarorin shirin nan nata da ke zuwa a kullum, watao “Gari ya Waye”, da kuma shirin mata, watao “Mata a Yau” domin gabatar da jerin tattaunawa, da hira da wasu manyan likitoci, masu bada shawarwari da kuma sauran kwararru a bangaren lafiya, game da matsalolin da suka danganci lafiyar kwakwalwa a Arewacin Najeriya. Duk da cewa kwararu sun tabbatar da cewa lafiyar kwakwalwa wani mahimmin bangare ce ga lafiyar jiki da kasancewa cikin koshin ladiya, said ai an yi watsi da ita a Arewacin Najeriya da ma Najeriya baki daya.
Kamar yadda Kungiyar Likitocin Kwakwalwa ta Najeriya (APN) suka bayyana, cewa sama da ‘yan Najeriya milyan 60 ne ke fama da matsalolin lafiyar kwakwalwa, amma kaso 10 cikin dari ne kacal suke iya samun kulawar da ta kamata. Shugaban kungiyar likitocin ta APN, Taiwo Obindo ya bayyana cewa gibin da ake da shi wajen samun magani shi ne ya haifar da matsaloli da dama, da suka hada da rashin ilimin abin, wanda kuma hakan ya bar mutane da karancin bayanai game da abubuwan da ke haddasa matsalolin lafiyar kwakwalwa, da kasa gane su da kuma neman kulawar da ta dace.
Duk da tsananin da matsalolin lafiyar kwakwalwa suka yi a kasar nan, kamar yadda kungiyar likitoci ta Najriya ta bayyana, likitoci 350 ne kadai ke aiki a halin yanzu a Najeriya, wadda ke da adadin mutane milyan 220. A kiyasta cewa a kalla daya daga cikin kowanne mutum hudu a Najeriya yana rayuwa ne da wani nauyi na larurar kwakwalwa.
“Mutane basu fahimci abin da ya shafi lafiyar kwakwalwa ba,” kamar yadda wata kwararriya a fannin lafiyar kwakwalwa a Najeria, Aisha Bubah ta bayyana. Ta ce, “Don haka ne ake danganta lafiyar kwakwalwa da abubuwa da suka danganci al’adu, chamfe-chamfe da kuma tsafi. Sannan yadda ake tunanin mutanen da ke da lafiyar kwakwalwa a koda yaushe shi ne tunanin sai wadanda yanayin su ya ta’azzara.”
AREWA24 tana aiki domin cike wawakeken gibin ilimi ta hanyar bayar da mahimman bayanai da wayar da kai game da kula da lafiyar kwakwalwa, da larurorin kwakwalwa da kuma cikakkiyar lafiyar kwakwalwa. Manufar wannan shiri na gangamin lafiyar kwakwalwa da AREWA24 ta shirya shi ne ta cike gibin bayanan da ba a samu, ta hanyar samar da ingantattun bayanai da kuma kawar da nuna kyama da ke tattare da matsalolin lafiyar kwakwalwa. AREWA24 ta tattaro gamayyar rukunin masana lafiyar kwakwalwa, masu bada shawarwari da kwararru kana bin da ake Magana a kai, wadanda za su tattauna yadda za mu samar da wasu hanyoyi domin kula da lafiyar kwakwalwa, a daidaikunmu da kuma tare iyalanmu. Wannan ya hada da aiyuka, kama daga duba mara lafiya, gano cutar da ke damunsa, bashi magani da kuma shawarwari – duk domin kula da kuma dawo da koshin lafiyar kwakwalwar al’ummar Arewacin Najeriya.
“A AREWA24, mun mayar da hankali don yin amfani da sananniya, amintacciya kuma shararriyar tasharmu mai nishadantarwa domin hidimtawa al’ummar Arewacin Najeriya da gamgami masu alfani kamar wannan gangami namu da ke tafe “Watan Mayar da Hankali Kan Lafiyar Kwakwalwa”, ta bakin Aisha Lawal, babbar shugaba mai kula da Shirye-shiryen AREWA24 na dakunan shirye-shirye. Ta ce “Mun yi Imani wannan wani nauyi ne na al’umma a kanmu mu samar da musu da abin da ya fi nishadantar da masu kallo kawai. Shi yasa mu ke so mu wayar da kai a kan mahimman batutuwa a cikin al’ummarmu kamar abin da ya shafi lafiyar kwakwalwa. Muna so mu taimaka wajen ilimantarwa da fadakar da ‘ya’yanmu maza da mata, don taimaka musu su yi kyakkyawar rayuwa a nan gaba, da kuma kokarin magance abubuwan da ke jawo talauci, wanda tabarbarewar bangaren kula da lafiyar kwakwalwa ke bada gagarumar gudunmawa.”
GAME DA TASHAR AREWA24: Tahsar AREWA24 da shirye-shiryenta, an kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, tashar AREWA24 tana kaiwa ga mutane sama da milyan 40 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma yammacin nahiyar Afirka a kan tauraron dan dan’adam na Eutelsat da ke kan tsarin kallo kyauta, da kuma kan tauraron dan adam na StarTimes da ke kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ke kan tsarin biya kudi, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101), da kuma tauraron dan adam na Canal+ a kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba #285) a Jamhuriyar Nijar, da Chadi da kuma Kamaru. AREWA24 na amfana da masu kallo da ke kasancewa da dukkanin shafukanta na yanar gizo a kan AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, da Instagram.com/AREWA24channel. Haka kuma AREWA24 tana yada shirye-shiryenta a tsarin kallo kai tsaye a ko ina a duniya a kan AREWA24 On Demand tare da hadin guiwar Vimeo.
Domin samun damar kallo kai tsaye a ko ina a duniya a kan AREWA24 ON DEMAND, ku shiga http://tv.arewa24.com ko ku sauke manhajar daga kan IOS App Store, ko Google Play, ko Apple TV, ko Roku Channel Store da kuma Amazon Fire TV.
Domin karin bayani, sai ku tuntubi: info@arewa24.com
Post Views: 2,674 -
AREWA24 na sanar da sabon jadawalin shirye-shirye na wasannin kwaikwayo da take shiryawa, da fina-finai, da shirye-shiryenta na cikin gida a yayin da kamfanin ke cika shekaru 10 da kafuwa
AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba wajen yaɗa shirye-shirye masu nishaɗantar da iyali da tsarin rayuwa cikin harshen Hausa, wadda ke da ofishin samar da shirye-shirye a Najeriya da yammacin Afirka, tana sanar da wani gagarumin sabon jadawali na shirye-shirye, da fina-finai da wasannin kwaikwayo da take shiryawa da kuma karɓar wasannin kwaikwayo na Hausa masu dogon zango domin nuna su a mahajarta ta kallo kai tsaye, wato AREWA24 On Demand.
Domin bukin murnar cikar AREWA24 shekaru 10, tashar ta kaddamar da sabon shirinta na matasa, wato, “Arewa Gen-Z,” wanda aka shirya domin matasan Arewacin Najeriya masu ɗinbin yawa. Matasa ne ke shirya wa, kuma gabatar da shirin “Arewa Gen-Z”, wanda ke mayar da hamkali a kan irin ƙalubalen da a yanzu matasa ke fama da shi kowacce rana. Shirin na mintuna 30 da ake gabatarwa a kowanne mako, zai dinga kawo labarun nasarori, da fasaha, da waƙe-waƙe, da kuma al’adun matasa. Shirin zai kasance wata farfajiya domin abubuwan da aka san matasa da shi domin jawo hankalin matasa a faɗin Arewacin Najeriya.
Haka kuma nan ba da daɗewa ba AREWA24 za ta fito da fim ɗinta na farko mai gajeren zango, mai sunan, “The Jaru Road,” wani labari mai ƙayatarwa kuma na asalin Arewacin Najeriya, wanda aka shirya da harshen Turanci, kuma domin masu kallo dake fadin Afirka da ma sauran sassa na duniya. Kamfanin ya tsara shirya ƙarin wasu fina-finai huɗu a 2024 – 2025, wasu da harshen Hausa domin masu kallo a Najeriya da kuma Yammacin Afirka, wasu kuma da harshen Turanci domin masu kallo a dukkanin faɗin Afirka da duniya baki ɗaya. Bugu da ƙari, AREWA24 za ta ƙaddamar da shirin “Climate Change Africa,” wani shiri da zai yi duba kan tasirin da sauyin yanayi yake yi a Najeriya, da faɗin Afirka, da sauran sassan duniya baki ɗaya.
“Waɗannan sabbin shirye-shirye suna nuna irin yadda AREWA24 ta mayar da hankali wajen samar da shirye-shiryenta na cikin gida da suke da alaƙa da halin da al’umma ke ciki, da wasannin kwaikwayo, da kuma fina-finai, sannan bisa matakin ingancin shirye-shirye a duniya.” A ta bakin Shugaban Sashen Kasuwanci da Tallace-tallace kuma Mataimakon Shugaban AREWA24, Celestine Umeibe, ya bayyana cewa “waɗannan sabbin shirye-shirye suna nuna yadda muke iya samar da shirye-shirye masu ƙayatarwa domin masu kallonmu na cikin gida, da kuma shirye-shiryen da za su kai har zuwa kasahen duniya, da kuma nunawa sauran masu kallo na nahiyar Afirka da faɗin duniya yadda asalin rayuwar Arewacin Najeriya da Yammacin Afirka take.”
Tashar AREWA24 za ta cigaba da samar da sabbin zango na fitattun wasannin kwaikwayonta da take shiryawa, wato “Kwana Casa’in da kuma “Dadin Kowa,” sannan tana kan aikin samar da wasu sabbin wasannin kwaikwayo masu dogon zango guda uku da za fito a ƙarshen shekarar 2024 da kuma cikin shekarar 2025. Na farko a cikin sabbin wasannin kwaikwayon masu dogon zango shi ne, “Jos Chronicles,” wanda aka tsara a yankin jahohin tsakiyar kasarnan a Birnin Jos, kuma za a shi ne da Harsunan Turanci da kuma Hausar Jos. Shirin wasan kwaikwayo ne da ya ƙunshi barkwanci – wanda zai mayar da hankali a kan alaƙa mai sarƙaƙiya da ke tsakanin wasu abokai biyar, kuma ana sa rai zai jawo hankalin masu kallo daga yankin jahohin tsakiyar Najeriya. Haka kuma AREWA24 za ta dora wannan wasan kwaikwayo na “Jos Chronicles” a kan mahajarta ta kallo kai tsaye domin masu kallo talabijin a faɗin Afirka da kuma duniya baki ɗaya.
Haka kuma, AREWA24 tana aikin haɗin guiwa da manyan masu shirya fina-finan Hausa na Kannywood da dama domin ɗora wasannin kwaikwayonsu masu dogon zango a kan manhajar AREWA24 ON Demand da kuma tashar AREWA24 television network.GAME DA AREWA24 (https://arewa24.com/company-overview/): AREWA24 da Bangarenta na samar da shirye-shirye, An fara gabatar da shiryen shiryen AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen Hausa masu inganci, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, tashar AREWA24 tana kaiwa ga mutane sama da milyan 40 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma Yammacin Afirka a kan tauraron dan dan’adam na Eutelsat da ke kan tsarin kallo kyauta, da kuma kan tauraron dan adam na StarTimes da ke kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ke kan tsarin biya kudi, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 136), da kuma tauraron dan adam na Canal+ a kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba #297) a Jamhuriyar Nijar, da Chadi da kuma Kamaru, AREWA24 na amfana da masu kallo da ke kasancewa da dukkanin shafukanta na yanar gizo a kan AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, da Instagram.com/AREWA24channel. Haka kuma AREWA24 tana yada shirye-shiryenta a tsarin kallo kai tsaye a ko ina a duniya a kan AREWA24 On Demand tare da hadin guiwar Vimeo.
Domin samun damar kallo kai tsaye a ko ina a duniya a kan AREWA24 ON DEMAND, ku shiga http://tv.arewa24.com ko ku sauke manhajar daga kan IOS App Store, ko Google Play, ko Apple TV, ko Roku Channel Store da kuma Amazon Fire TV.
Domin karin bayani, sai ku tuntubi: info@arewa24.comPost Views: 1,650 -
Ina ma ‘KWANA CASA’IN’ na AREWA24 ya zama abin koyi
Fim din Kwana Casa’in, wato shirin Hausa dirama ne da a ke nunawa a tashar talabijin ta AREWA24, inda zubi da tsarin labarin ya sha bamban da finafinan da mu ka saba kallo, wanda ba su wuce tunanin yaro karami ba.
Labarin ya na magana ne a kan siyasar kasar nan da irin abubuwan da ke faruwa a jami’o’inmu da ma rayuwa ga bakidaya.
Tuntuni ya kamata a rika zakulo irin wadannan matsaloli, saboda su ne damuwarmu, amma sai finafinan da a ke kira na Hausa su ka duge ga rawa da waka da gasar nuna jiki da matsattsun wanduna.
A ciikin Kwana Casa’in, tsarin hoto kansa na daban ne, domin ya sha bamban da irin tsarin hoton da mu ka saba gani, saboda an yi amfani da na’urar daukar hoto mai matukar inganci ta yadda mai kallo zai ga kamar a gabansa abubuwan ke faruwa.Wuraren da a ka yi amfani da su irinsu asibitoci, ofisoshi, gidaje, makarantu ko gidan rediyo, nan ma abin jinjinawa ne, domin kuwa an yi amfani da wuraren da su ka dace ta yadda duk wanda ba dan kasa ba, idan ya kalla, zai ga tsantsar kama da gaskiya a cikin labarin, wanda hakan ma iyawa ce. Idan na nutsu Ina kallon Kwana Casa’in sai na ji tamkar gaske ne. Yadda masu mulki ke rayuwa da rayuwar talaka a wannan zamani da yadda a ke amfani da talaka, domin kama madafun iko duk an bayyanar da shi. Ina da yakinin kafin labarin ya kare mutane da dama za su dauki darasin rayuwa. Lokacin da na ga hotunan wasu jaruman Kannywood a cikin Kwana Casa’in kafin na fara kallon fim din, sai da na ji jiki na ya yi sanyi, saboda Ina tsoron kar su bata dirimar ta yadda za mu rika kallon ta kamar shirme, amma abin da ya burge ni shi ne yadda su ka shiga su ka bata a cikin shirin ba tare da kawo mishkila ko mayar da abin wasan yara ba. Hakan ya nuna ma ni kenan da za su sami labari mai inganci da kayan aiki, sannan su sako masu ilimin a cikin nasu shirye-shiryen, kila su ma za su samu su mike a Kannywood din kenan. Yadda jaruman su ka nuna dagiya da tsantsar kwarewa sosai, ya yi kyau matuka ta yadda ko wadanda su ka saba kallon finafinan kasashen ketare za su jinjina masu domin kasashen da su ka cigaba su na shirya dirama mai dogon zango ko finafinai kan matsalar da su ke fuska a kasar fiye da shirme irin wanda a ke yi a finafinan da mu ka saba gani. Da alama dai Kwana Casa’in shi ne labarin da ya ke kokarin taushe shirin dadin Kowa na Arewa 24 din dai, domin kamar yadda a ka kasa samun wani shirin dirama da zai yi karo da Dadin Kowa daga masana’antar Kannywood, watakila AREWA24 din ce dai kadai za ta iya yin karo shi da wannan sabon shiri tsararre na Kwana Casa’in. Tsawon lokacin da na dauka Ina kallon shirin Hausa na Kannywood lallai na gano wa Kannywood makarantar da za su kara ilmi. Sannu a hankali AREWA24 za ta maye gurbin shirin Hausa dirima, saboda su ne su ke tattauna abinda ya dame mu a kasa, ba rawa da juyi gaban allunan talabijin ba. Fadila H Aliyu Kurfi marubuciya ce mai sharhi kan al’amuran yau da kullum kuma ’yar gwagwarmaya.
Za a iya samun ta a imel: fadilakurfi@gmail.com ,
Facebook: Fadila H Aliyu Kurfi.
Read More at: https://hausa.leadership.ng/2019/04/18/ina-ma-kwana-casain-na-arewa-24-yazama-abin-koyi/Post Views: 9,639