Kamfanin Startimes da ke yada tashoshin talabijin na tauraron dan Adam, ya sanar da sanya fitacciyar tashar nan ta harshen Hausa wato AREWA24 cikin jerin tashoshin da ke kan
dikodarsu, a wani yunkuri da tashar ke yi na ganin ta biya bukatun dinbun mutanen da ke kallonta. A ta bakin Daraktan kasuwanci na tashar, Qasim Elegbede ya bayyana cewa “bukatar samar da karin tashoshin talabijin na harshen Hausa ta ci gaba da hauhawa a tsakanin masu kallo musamman ma a arewacin Najeriya a shekarar da ta gabata. Kasancewar mu na sauraron bukatun al’umma, mu na kokari ne mu ga mun bawa masu kallonmu hakikanin abin da su ke bukata, da karin shirye-shirye masu nishadantarwa.”
Shi ma da ya ke bayani game da wannan ci gaba da aka samu, shugaban sashen gudanar da tallace tallace na tashar AREWA24, Celestine Umeibe, ya yi nuni da cewa “hakika hadin guiwa tsakanin AREWA24 da kamfanin Startimes wani ci gaba ne da ake bukata. A yanzu mutane da dama masu magana da harshen hausa a Arewacin Najeriya da ma sauran sassan kasar zasu samu damar kallon shirye-shiryen tsarin rayuwa da nishadantarwa dake nuni da al’adu daban-daban da ake alfahari da su a Arewacin Najeriya akan wannan tasha da ke kan tsarin biya.”
Ya kuma kara da cewa “A halin yanzu masu tallace-tallace da kamfanoninsu zasu iya kaiwa ga dukkanin mutanen da suke so su tallata musu hajarsu ta hanyar amfani da tashar AREWA24 wadda a yanzu take cikin dukkanin tsarikan da ke kan dikodar Startimes.”
Tashar Arewa 24 na nuna shirye-shiryen na nishadi da al’adu da kuma addinai cikin harshen hausa wadanda take yadawa akan tasha ta 138 akan Dikodar Startimes. Idan za a iya tunawa a wataan Disanmbar shekarar 2017 ne, Kamfanin Startimes ya sanar da fara nuna tashoshinsa a Maiduguri babban birnin Jahar Borno a wani gagarumin yunkuri da yake yi domin cika alkawarin da ya dauka na samar da shirye-shirye masu nishadantarwa cikin sauki a kowanne gida a Najeriya..
You Might also like
-
Al Jazeera da AREWA24 sun yi hadin guiwa don fassara shirye-shirye na musamman da masu dogon zango zuwa harshen Hausa domin masu kallo sama da milyan 40 dake arewacin Nijeriya da kuma yankin Sahel
23 ga watan Nuwamba, 2021. Doha/Lagos. Nan ba da jimawa ba masu kallon tashar AREWA24 sama da milyan 40 da ke Arewacin Najeriya, da kasashen Nijar, da Chad da kuma Cameroon za su fara kallon shirye-shirye Al Jazeera na musamman da masu dogon zango na turanci, da aka fassarasu zuwa harshen Hausa, bisa wata sabuwar yarjejeniya da aka cimma kwanannan tsakanin Al Jazeera da kuma AREWA24.
Wannan yarjejeniya za ta bada damar kallon shirye-shiryen Al Jazeera na harshen Turanci a kan tashar tauraron ta AREWA24 dake kan tsarin kallo kyauta da kuma sauran kafafen tauraron dan adam na yankin da ke kan tsarin biyan kudi na: DStv, da StarTimes, da CANAL+ da kuma TSTV sannan kuma da tsarin kallo kai tsaye ta yanar gizo daga ko ina a duniya ta manhajar AREWA24 wato “AREWA24 On Demand.”
“Mun ji dadi sosai da wannan yarjejeniya, kasancewar shirye-shiryen Al Jazeera na harshen turanci za su dinga zuwa ga sabbin masu kallo dake yanki mafi girma a nahiyar Afirka da harshensu,” a ta bakin Mai rike da mukamin Babban Darakta mai kula da Sashen Sadarwa da Al’amuran Kamfanin a Duniya, Ramzan Alnoimi. Ya kara da cewa “Muna kokari muga mun fadada hanyoyi yada shirye-shiryen Al Jazeera da aka fassarasu da sauran harsuna a nan gaba.”
Shugaban tashar AREWA24, Jacob Arback, ya bayyana cewa: Tashar Al Jazeera da kuma kayatattun shirye-shiryenta za su samu karbuwa sosai a wajen masu kallon tashar AREWA24 na Arewacin Najeriya da kuma yammacin Afirka.”
Ya kuma kara da cewa “Mun yi matukar jin dadi game da wannan hadin guiwa, da kuma kasancewarmu tashar talabijin ta farko da za ta yada shirye-shiryen Al Jazeera masu inganci da harshen Hausa, harshen da sama da mutane milyan 90 ke magana da shi a Najeriya da kuma Yammacin Afirka.
Tahsar AREWA24 da sashen shirye-shiryenta, an kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen hausa. Tashar AREWA24 taNA kaiwa ga mutane sama da milyan 40 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma yammacin nahiyar Afirka, sannan kuma kamfanin da ke da ofisoshinsa a Kano da kuma Lagos yana daga cikin kamfanonin ‘yan Afirka da ke kan gaba ta fuskar yada labarai, samar da shirye-shirye, da kuma yada shirye-shirye na talabijin.
Najeriya na daya daga cikin kasashen da aka fi kallon tashar Al Jazeera. Kai tsaye wannan yarjejeniya za ta bada damar fassara shirye-shiryen Al Jazeera zuwa harshen Hausa da kuma yada su ga daukacin masu kallo daga sassa daban-daban na yankin.
GAME DA TASHAR ALJAZEERA ENGLISH: Tashar harshen Turanci ta Al Jazeera tana gabatar da shirin labarun duniya da al’amuran yau da kullum da kuma sa mutane su san halin da ake ciki, wanda ya samo asali ta yin imani da cewa kowa yana da labarin da ya dace a saurara. Ta aikin jaridar da take yi na rashin nuna tsoro da kuma shirye-shiryenta da suka lashe labar yabo, tashar tana bada ingantattun labarai game da mutane a ko’ina, ba tare da la’akari da yankin da suka fito ko kuma al’adunsu ba. Tun daga lokacin da aka kaddamar da tashar a shekarar 2006, tashar Al Jazeera ta harshen Turanci ta samu yabo a fadin duniya bisa nuna rashin nuna son rai da kuma rahotanni na gaskiya, inda ta samu nasarar samun lambobin yabo daga bangarorin aikin jarida da aka fi girmamawa a duniya. Tashar da ke da babban ofishinta a yankin Gabas ta Tsakiya da kuma wakilai a ofisoshinmu 69 da ke fadin duniya, ta kuma dauki wani sabon salo ta fuskar labaran duniya. Daga kasuwannin da suka ci gaba zuwa kasuwannin da ke tasowa, tashar tana kara gundarin abin da ya shafi mutane ta hanyar kasancewa a wajen da abu ke faruwa a gurare da dama. A yau, tashar AlJazeera ta harshen Turanci tana kaiwa ga gidaje sama da milyan 350 a kasashe 150 (Daga watan Fabrairun 2020), inda take yada ingantattun rahotanni da ke fadakarwa, karfafa guiwa da kuma kalubalantar yadda ake kallon abubuwa.
Domin karin bayani, sai ku danna wannan https://www.aljazeera.com/
GAME DA TASHAR AREWA24: Tahsar AREWA24 da shirye-shiryenta, an kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, tashar AREWA24 tana kaiwa ga mutane sama da milyan 40 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma yammacin nahiyar Afirka a kan tauraron dan dan’adam na Eutelsat da ke kan tsarin kallo kyauta, da kuma kan tauraron dan adam na StarTimes da ke kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ke kan tsarin biya kudi, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101), da kuma tauraron dan adam na Canal+ a kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba #285) a Jamhuriyar Nijar, da Chadi da kuma Kamaru. AREWA24 na amfana da masu kallo da ke kasancewa da dukkanin shafukanta na yanar gizo a kan AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, Instagram.com/AREWA24channel, and twitter.com/AREWA24channel.
Domin karin bayani game da AREWA24 sai ku ziyarci https://arewa24.com/company-overview/ ko kuma ku tuntubemu ta wannan adireshi: info@arewa24.com
Post Views: 37,340 -
Tashar AREWA24 Tana Sanar Da Kaddamar Da Sabon Sashen Wasannin Kwaikwayo Da Fina-Finai Da take Shiryawa
AREWA24, tashar talabijin da ke kan gaba wajen yada shirye-shiryen nishadantar da iyali da tsarin rayuwa, wadda ke da ofishin daukar shirye-shiryenta a Najeriya a Yammacin Afirka, tana sanar da kaddamar da sabon sashen wasannin kwaikwayo da fina-finan da take shiryawa. Sabon sashen shirye-shiryen kamfanin zai samar da rubutun labaru da kuma shirya sabon jadawalin sabbin wasannin kwaikwayo masu dogon zango da kuma daidaikun fina-finai, don bada labarun Afirka na asali daga Arewacin Najeriya da kuma Yammacin Nahiyar Afirka da harshen Hausa da kuma na harshen Turanci zalla.
Ofishin samar da shirye-shiryen tashar AREWA24, ya kasance yana shiryawa da kuma yada kayatattu kuma shahararrun wasannin kwaikwayo masu dogon zango na Hausa a Arewacin Najeriya da Yammacin Afirka, wato “Dadin Kowa” wanda a halin yanzu ya kai zango na 25, da kuma wasan kwaikwayon tashar da ya kunshi siyasa, wato “Kwana Casa’in” (“90 Days”), wanda aka kammala daukar zango na 7 a kwanannan. Ana kan shirya wasu wasannin kwaikwayon masu dogon zango da dama, kuma wannan kamfani zai fara nuna shirin fim mai gajeren zango da ya shirya na farko a zango na hudu a shekarar 2022.
“AREWA24” ta kasance tana daga darajar wasu daga cikin kwararrun marubutan Najeriya, da masu shirya fina-finai, da daraktoci, da masu tace hotuna da kuma jarumai tun bayan kafuwar tashar shekaru takwas da suka gabata. Shugaban tashar AREWA24 Jacob Arback, ya bayyana cewa, “A halin yanzu muna matsayin babban kamfanin samar da shirye-shirye na ‘yan Afirka, mai samar da tsararrun shirye-shirye masu inganci na Afirka – domin ‘yan Najeriya, da ‘yan Afirka da kuma masu kallo da ke yammacin duniya, wadanda ke kara jin dadin kallon irin wadannan labaru masu kayatarwa da aka tsara su da inganci cikin wasannin kwaikwayo da fina-finai daga wannan nahiya”.
Shugaban sabon sashen wasannin kwaikwayon da fina-finai shi ne Evans Ejioju, wani gogagge kuma kwararre, da ya kasance a matsayin babban mai shirya shirin wasan kwaikwayon nan mai dogon zango na Kwana Casa’in tun daga zango na farko. Salisu Balabare, wanda ke bada umarni a shirin na Kwana Casa’in kuma wanda ya dade yana bada umarni a shirin wasan kwaikwayo nan mai dogon zango na Dadin Kowa, shi ne zai jagoranci bangaren kirkira na wannan sabon sashe. Bob Reid, sanannan da ya lashe lambar yabo ta Emmy-award a matsayin babban mashiryin shirin nan na kamfanin Discovery Networks, kuma tsohon mai kula da kimar ma’aikata (EVP), kuma babban shugaban sashen shirye-shirye a tashar The Africa Channel da ke kasar Amurka, shi ne zai kasance a matsayin mashawarci kuma babban mashiryin shiri na wasannin kwaikwayo da fina-finan da tashar AREWA24 ke shiryawa.
Samar da wannan sabon sashen na wasannin kwaikwayo da fina-finai, zai sa tashar AREWA24 ta amfani kwarewa da kuma kayan aikin shirye-shirye da ta tattara, sannan kuma ta nemi abokan hulda masu kaifin basira daga dukkanin fadin duniya, da kuma manyan kamfanonin da ke aikin yada shirye-shirye kai tsaye ta yanar gizo (streaming services) a duniya, domin bunkasawa da shirya rubutattun shirye-shirye.
“Manufarmu ita ce, shirya karin fitattu kuma kayatattun wasannin kwaikwayo domin masu kallonmu da ke magana da harshen Hausa”. Arback ya ce, “Wasu daga cikin shirye-shiryen da za mu samar, ba lallai a fara nuna su a tashar AREWA24 ba. A nan gaba, mun shirya samar da jadawalin shirye-shirye da suka dace da masu kallo a fadin nahiyar Afirka da kuma sauran sassa na duniya. Sabon sashen shirye-shiryen zai bamu dama mu tsara shirye-shiryenmu domin su dace da dukkanin masu kallo. Don yin hakan, mun tsara shirya shirye-shirye na ‘yan Afirka masu inganci da harshen Turanci da kuma harshen Hausa kuma mu tabo karin batutuwan da ke ciwa mutane tuwo a kwarya a cikin nau’ikan shirye-shirye da dama.”
GAME DA TASHAR AREWA24: Tahsar AREWA24 da bangaren shirye-shiryenta, an kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen Hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kade-kade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, tashar AREWA24 tana kaiwa ga mutane sama da milyan 40 masu magana da harshen Hausa a Najeriya da kuma yammacin nahiyar Afirka a kan tauraron dan dan’adam na Eutelsat da ke kan tsarin kallo kyauta, da kuma kan tauraron dan adam na StarTimes da ke kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba 138), da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ke kan tsarin biya kudi, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101), da kuma tauraron dan adam na Canal+ a kan tsarin biyan kudi (tasha mai lamba #285) a Jamhuriyar Nijar, da Chadi da kuma Kamaru. AREWA24 na amfana da masu kallo da ke kasancewa da dukkanin shafukanta na yanar gizo a kan AREWA24.com, facebook.com/AREWA24, Instagram.com/AREWA24channel. AREWA24 tana kuma yada shirye-shirye kai tsaye ta yanar gizo a duniya a kan manhajar nan ta, AREWA24 On Demand tare da hadin guiwar kamfanin Vimeo.
Domin yin rijista da manhajar kallon shirye-shirye kai tsaye ta yanar gizo a kan manhajar AREWA24 ON DEMAND, sai ku ziyarci http://tv.arewa24.com ko kuma ku sauke manhajar daga IOS App Store, Google Play, Apple TV, Roku Channel Store da kuma Amazon Fire TV.
Domin karin bayani, sai ku tuntubi: info@arewa24.com
Post Views: 10,216 -
AREWA24 na bikin cikarta shekaru shida tare da gabatar da sababbin shirye-shirye
Tashar AREWA24, Tashar talabijin ta Hausa dake kan gaba wajen samar shirye-shirye masu nishadntarwa da nuna tsarin iyali, wadda ke da dakin daukar shirye-shirye a Najeriya dake Yammacin Nahiyar Afirka, tana sanar da wani sabon jadawalin shirye-shirye da kuma kayatattun shirye-shirye domin su dace da bukin cika shekaru shida da kafuwar wannan tasha.