Shirin “The 77 Percent” – Shirin Talabijin ne da DW ta shirya domin matasa – wanda tashar AREWA24 da ke Najeriya ta fassarashi zuwa harshen Hausa. Kamar yadda masu daukar nauyin shirin suka bayyana a ganawar su da manema labarai, tashar AREWA24 za ta nuna wannan shirin da harshen Hausa a lokutan da aka fi kallon tashar.
Shirin “The 77 Percent” ya samo sunansa ne daga kason matasan Afirka ‘yan kasa da shekaru 35, sannan aka tsara shi domin nuna rayuwarsu tare da “labarun mahimman abubuwan da suka fuskanta a rayuwarsu”. Shirin na tsawon mintuna 30, an taba nuna shi ne a baya da harsunan turanci da Portuguguese.
Shugaban tashar AREWA24 Jacob Arback, yayin da yake bayani game da karbar shirin, ya bayyana cewa,”Kara shirin “The 77 Percent” a cikin tsarin jadawalin shirye-shiryenmu wata babbar dama ce ga tashar AREWA24 wajen nuna batutuwa na zahiri, da kalubale da labarum nasarori daga matasa a kowanne bangare na fadin wannan nahiya. Muna alfahari da farin ciki da hadin guiwa tare da DW da kuma sadar da wannan shiri mai inganci ga matansamu masu magana da harshen Hausa da kuma iyalansu.”
Daraktan shirye-shiryen Afirka na DW, Claus Stacher, yayin da yake bayani game da kaiwar shirin kashi na 50 a wannan, ya bayyana cewa: “Mun tsara shirinmy ta yadda rukunin matasan da muka yi wannan shiri domin su za su fahimci shirin a matsayin shiri mai kayatarwa, da tsari sannan kuma an yi shi don ‘yan asalin nahiyar Afirka. Tsarin ‘yan Afirka, da tattaunawa da kuma samo mafita yana kara daraja ga abokan hadin guiwarmu na kafafen yada labarai na zamani, da radiyo da talabijin a wannan yanki. Muna da da tabbacin cewa wannan hadin guiwa da tashar talabijin kamar tashar AREWA24 zai kara budede kofofin samun hadin guiwa a nan gaba.
Tushi: DW.COM
You Might also like
-
AREWA24 Ta Kaddamar Da Sabon Dakin Shirye-Shirye
Tashar AREWA24tashar da ta yi fice wajen nishadantarwa da tsarin rayuwa da harshen Hausa a Kasar Nijeriya, na sanar da ku cewa, ta bude sabon Dakin Yada Shirye-shiryenta mai dauke da tsarika irin daban-daban da wasu sababbin shirye-shirye da za a fara a zango yada shirye-shiryenta karo na biyu. Sabon Dakin Yada shirye-shiryen zai taimakawa sabon salon shirin GARI YA WAYE da sabon salon shirin Sharhin Wasanni wato (Sport Central) da kuma sabon Salon Kayataccen shirin KUNDIN KANNYWOOD har ila yau, da SHARHIN FINA-FINAN KANNYWOOD. haka kuma, Tashar zata sake kawo muku shirin dake tattaunawa a kan lafiya da Cututtuka da Magani a cikin wani sabon salo da mai gabatar da shirin Lafiya Jari wanda za a rika gabatar da shi a Garin Abuja. wanda zamu karkare wannan sabon zango na uku na shirye-shiryen Nishadantarwa da kuma tsarin rayuwa da shirin ‘Haske; Matan Arewa’ wanda zai sada ku da shaharrrun matan Arewacin Nijeriyu. haka kuma, Tashar AREWA24 zata gabatar muku da sababbin Fina-finan Kannywood har karshen wannan shekara.
Bugu da kari, dan gane da sababbin shirye-shirye da Tashar AREWA24 ke kawo wa masu kallo, Tashar AREWA24 za ta kawo wa masu kallon sabbabin Fina-finan daga tashar ‘Zee World Series’ ‘Bhagya Lakshmi’ da wani fitaccen sabon Wasan Kwaikwawo daga Kasar ‘Turkish’ “Prisoner of love’ wato ‘Tarkon Kwana’ da wasu sabbabbin Fina-finan Kasar Indiya. kamar dukkaninn shirye-shiryen kasashen ketare masu lasisi na Tashar AREWA24. duk wadannan guntattakin Fina-finan na Series da na Fina-finan Indiya ana daukarsu ne da shiryasu da Harshen Hausa a Daikin daukar Sauti na Tashar AREWA24.
Babbar Mai Gabatar da Shirye-shiryen ‘GARI YA WAYE’ Aisha Lawal ta ce, ‘Masu Kallon Tashar AREWA24 sun cancanci a gabatar musu da kyawawan shiri da zai birge su, kuma ba dare ba rana mun kwashe wata da watanni muna ta aiki tukuru don ganin mun kawata sabon Dakin Yada shirye-shiryenmu mai fasali daban-daban. Sabon shirinmu na ‘Gari ya Waye’ ba zai tsaya ga sakawa masu kallo da sabon salon gabatar da shirin ka dai bane, Amma, har da saka musu da sabbabin masu gabatar da shirin wato Nana Musa da kuma Muhammad Abubakar Suleiman.’ An kafa tashar AREWA24 a Shekara ta 2014 domin cike gagarumin gibin samar da shirye-shirye masu nishadantarwa da tsarin rayuwa a Harshen Hausa, wadanda su ke nuna hakikanin rayuwa a Arewacin Najeriya, da Al’adu da Kade-Kade da Fina-Finai da Fasahar zane da Girke-Girke da kuma Wasanni. A yau, sama da mutane miliyan 80 masu magana da Harshen Hausa a fadin Najeriya da makwabtansu na Yammacin Afirika na kallon Tashar AREWA24 da ake haskawa a kan Tauraron Dan Adam ta Eutelsat a kyauta, a Kasa Najeriya kuma, ana iya kama ta a kan Dikodar Tsarin biya ta StarTimes Tasha ta 138 da kuma Dikododin Kamfanin Multichice masu guda biyu masu Tsarin Biya wato DSTV Tasha ta 261 da kuma GOtv Tasha ta 101.
GAME DA AREWA24: Tashar AREWA24 ( arewa24.com) tasha ce ta farko a kasar nan kuma tashar daya tilo dake shiryawa da kuma yada shirye-shiryenta a kan Tauraron Dan Adam cikin harshen Hausa Wadda kuma aka sadaukar da ita don nishadantar da iyali, Tashar AREWA24 ta Mayar da hankalin wajen bunkasa da yada shirin talabijin da harshen Hausa, domin cike gibin da masu magana da harshen Hausa ke fuskanta a fadin duniya, wadanda da yawansu ke dawowa kallon Tashar AREWA24 ta hanyar amfani da Manhajar Yanar Gizo a matsayin wata hanya da zata sada su da Al’adunsu da kuma Al’ummun Duniya.
Ana saka Shirye-shiryen Tashar AREWA24 a kowanne mako a kan shafin Youtube.com/Arewa24channel, haka kuma tashar tana samun matukar karuwa ta hanyar tattaunawa da masu kallonta a shafukanta na sada zumunta kamar Arewa24.com da Facebook.com/AREWA24 da Instagram.com/AREWA24channel da kuma twitter.com/AREWA24channel
Don karin bayani, sai ku tuntubemu a info@arewa24.com
Post Views: 8,995 -
Ina ma ‘KWANA CASA’IN’ na AREWA24 ya zama abin koyi
Fim din Kwana Casa’in, wato shirin Hausa dirama ne da a ke nunawa a tashar talabijin ta AREWA24, inda zubi da tsarin labarin ya sha bamban da finafinan da mu ka saba kallo, wanda ba su wuce tunanin yaro karami ba.
Labarin ya na magana ne a kan siyasar kasar nan da irin abubuwan da ke faruwa a jami’o’inmu da ma rayuwa ga bakidaya.
Tuntuni ya kamata a rika zakulo irin wadannan matsaloli, saboda su ne damuwarmu, amma sai finafinan da a ke kira na Hausa su ka duge ga rawa da waka da gasar nuna jiki da matsattsun wanduna.
A ciikin Kwana Casa’in, tsarin hoto kansa na daban ne, domin ya sha bamban da irin tsarin hoton da mu ka saba gani, saboda an yi amfani da na’urar daukar hoto mai matukar inganci ta yadda mai kallo zai ga kamar a gabansa abubuwan ke faruwa.Wuraren da a ka yi amfani da su irinsu asibitoci, ofisoshi, gidaje, makarantu ko gidan rediyo, nan ma abin jinjinawa ne, domin kuwa an yi amfani da wuraren da su ka dace ta yadda duk wanda ba dan kasa ba, idan ya kalla, zai ga tsantsar kama da gaskiya a cikin labarin, wanda hakan ma iyawa ce. Idan na nutsu Ina kallon Kwana Casa’in sai na ji tamkar gaske ne. Yadda masu mulki ke rayuwa da rayuwar talaka a wannan zamani da yadda a ke amfani da talaka, domin kama madafun iko duk an bayyanar da shi. Ina da yakinin kafin labarin ya kare mutane da dama za su dauki darasin rayuwa. Lokacin da na ga hotunan wasu jaruman Kannywood a cikin Kwana Casa’in kafin na fara kallon fim din, sai da na ji jiki na ya yi sanyi, saboda Ina tsoron kar su bata dirimar ta yadda za mu rika kallon ta kamar shirme, amma abin da ya burge ni shi ne yadda su ka shiga su ka bata a cikin shirin ba tare da kawo mishkila ko mayar da abin wasan yara ba. Hakan ya nuna ma ni kenan da za su sami labari mai inganci da kayan aiki, sannan su sako masu ilimin a cikin nasu shirye-shiryen, kila su ma za su samu su mike a Kannywood din kenan. Yadda jaruman su ka nuna dagiya da tsantsar kwarewa sosai, ya yi kyau matuka ta yadda ko wadanda su ka saba kallon finafinan kasashen ketare za su jinjina masu domin kasashen da su ka cigaba su na shirya dirama mai dogon zango ko finafinai kan matsalar da su ke fuska a kasar fiye da shirme irin wanda a ke yi a finafinan da mu ka saba gani. Da alama dai Kwana Casa’in shi ne labarin da ya ke kokarin taushe shirin dadin Kowa na Arewa 24 din dai, domin kamar yadda a ka kasa samun wani shirin dirama da zai yi karo da Dadin Kowa daga masana’antar Kannywood, watakila AREWA24 din ce dai kadai za ta iya yin karo shi da wannan sabon shiri tsararre na Kwana Casa’in. Tsawon lokacin da na dauka Ina kallon shirin Hausa na Kannywood lallai na gano wa Kannywood makarantar da za su kara ilmi. Sannu a hankali AREWA24 za ta maye gurbin shirin Hausa dirima, saboda su ne su ke tattauna abinda ya dame mu a kasa, ba rawa da juyi gaban allunan talabijin ba. Fadila H Aliyu Kurfi marubuciya ce mai sharhi kan al’amuran yau da kullum kuma ’yar gwagwarmaya.
Za a iya samun ta a imel: fadilakurfi@gmail.com ,
Facebook: Fadila H Aliyu Kurfi.
Read More at: https://hausa.leadership.ng/2019/04/18/ina-ma-kwana-casain-na-arewa-24-yazama-abin-koyi/Post Views: 9,465 -
AREWA24 ta kaddamar da sabon jadawalin shirye-shiryenta na zango
Tashar AREWA24, tashar Hausa da ke kan gaba wajen nishadantarwa da tsarin rayuwa a Najeriya, tana sanar da fitowar jadawalin sabbin shirye-shiryenta na zango na hudu a wannan shekara da kuma zangon farko na shekarar 2019, wanda ya kunshi sabon wasan kwaikwayon tashar da aka dade ana jira, wanda zai zo a watan Janairu, kari a kan wasan kwaikwayon “Dadin Kowa” da tashar ke nunawa a halin yanzu wanda ta dade tana nunawa wanda kuma ya samu lambar yabo. A halin yanzu ana nan ana shirya wannan sabon wasan kwaikwayo mai kayatarwa, kuma ana tsammanin zai kawo wani sabon sauyi da inganci a bangaren shirye-shiryen talabijin da harshen Hausa.
Sabon jadawalin shirye-shiryen tashar AREWA24 da zai fara a watan Oktoba, ya kunshi shirin “Amo daga Arewa”. Wannan shiri na kade-kade ya kunshi gabatar da wakoki kai tsaye da tattaunawa da fasihan mawaka daga fadin Arewacin Najeriya, da suka hada da mawakan gargajiya da na R&B da masu wakokin sanyaya ruhi da kuma mawakan addinai. Shirin “Amo Daga Arewa” ya tattara kada-kaden gargajiya na al’ada da dama da yankin Arewacin Najeriya ke da su, kari a kan shahararrun shirye-shiryen AREWA24 na
Hip Hop.
A zangon na hudu , shirin nan na “Matasa@360” zai sake dawowa da wani sabon salo da kuma sabbin masu gabatarwa. Shirin na “Matasa@360” shiri ne na matasa da yayi daidai da zamani kuma yake bi lungu da sako, tare da mayar da hankali a kan basira da kirkira da kuma fasahar matasan Arewacin Najeriya.
Haka kuma shirin zai dinga tattauna kalubale na zahiri da matasan yankin ke fuskanta da kuma wahalhalun da suke fama da su a yau da kullum. Bangarorin da shirin ya kunsa za su nuna yadda matasan Arewacin Najeriya ke rayuwarsu ta yau da kullum, da alakarsu da sauran mutane, da kafafen yada labarai, da sana’o’i, da wasanni, da al’amuran yau da kullum, da rayuwar makaranta, da fasaha da sauran bangarorin da matasa daga dukkan fadin duniya ke da alaka da su.Haka kuma tashar AREWA24 za ta fara gabatar da shirin “Haske: Matan Arewa” kashi na hudu, wanda jajirtattun mata daga Arewacin Najeriya ke bayyana labarinsu cike da kwarin guiwa. Suke kuma bijirewa wasu dabi’u na zamantakewa da al’adu don su zamo shugabanni, ko yan kasuwa, ko masu sana’o’i, ko masu wayar da kai a yankunan karkara, ko masu shirya fina-finai da sauransu, Wadannan hazikan mata kan bayyana ci gabansu, da fadi-tashinsu, da matsalolin da suke fuskanta, da kuma nasarorinsu.
Cikon sabbin shirye-shiryen da tashar AREWA24 za ta gabatar a zango na hudu a wannan shekarar su ne sabbin fitattun fina-finan Kannywood daga kwararrun daraktocin masana’antar. A yanzu tashar AREWA24 ta yi fintinkau ga kowacce tasha dake yankin Arewa, idan ana magana a kan nuna fitattun fina-finan Kannywood.Sannan kuma tashar ta samar da shirye-shirye don manyan gobe da ke kallon shahararrun shirye-shiryen yara a tashar safe da yamma.
Haka kuma tashar tana sanar da daukar manyan kuma kwararrun ma’aikatan shirye-shirye da ta yi a dakin shirye-shiryenta da ke Kano: wato Kadiri Yusef da Evans Ejiogu, wadanda kowannensu ya zo da irin kwarewar da ya dade yana samu da irin shuhurar da ya yi a fagen shirin talabijin da kafafen yada labarai a Lagas, zuwa kano.
Kadiri Yusef dai wani babban ma’aikacin shirye-shirye ne a gidan talabijin na Silverbird Television, inda ya yi aiki tun daga shekarar 2004 zuwa 2017. Kadiri ya zamo shugaban sashen shirye-shirye na tashar Silverbird Television a shekarar 2006 inda ya bada umarni a manyan shirye-shiryen Silverbird da suka ciri tuta, da kuma dukkanin shirye-shiryenta na kai-tsaye. A tashar AREWA24, shi ne mai kula da bangaren bada umarni da tsara dukkanin shirye-shirye daban-daban da ake gabatarwa a dakin shirye-shirye.
Evans Ejiogu ya kasance kwararren mai samar da shirye-shiryen talabijin, mai shiryawa, mai bada umarni, marubuci sannan kuma mai tace hotunan bidiyo. Baya ga wannan gogewa da kwarewa a fagen daukacin nau’ikan shirye-shirye da yake da su, Evans ya kawowa tashar AREWA24 dabarun kasuwanci da ya samu a tsawon shekarun da ya shafe a fagen sadarwa da tallace-tallace. Evans yayi aiki a babban dakin gabatar da shirye-shirye , da wasan kwaikwayo na talabijin, da gajerun fina-finai, da tallace-tallace, da gidan radiyo da kuma shafukan yanar gizo, inda yake taimakawa wajen kawo babban matakin kwarewa da inganta shirye-shirye a tashar AREWA24.Babban Shugaban tashar AREWA24 Jacob Arback ya bayyana cewa, “Mun yi gagarumar sa’ar samun manyan ma’aikata da ke da irin wannan kwarewa da gogewar aiki don yin aiki a tashar AREWA24. Evans da Kadiri ba su tsaya iya bada gudunmawa ga jajirtattun ma’aikatanmu na shirye-shirye da suka tarar da kuma daga darajar shirye-shiryen tashar ba, suna kuma taimakawa wajen bunkasa bangaren aiyukan talabijin da kafafen yada labarai na Arewaci Najeriya.”
GAME DA TASHAR AREWA24: An kafa Tashar AREWA24 a shekarar 2014 domin cike wawakeken gibin da ake da shi a fagen shirye-shiryen nishadi da tsarin rayuwa da ake shiryawa da harshen hausa, wadanda ke nuni da abubuwan da ake alfahari da su a rayuwar Arewacin Najeriya, da al’adu, da kadekade, da fina-finai, da fasaha, da girke-girke da kuma wasanni. A yau, mutane masu Magana da harshen hausa sama da milyan 80 a Najeriya da kuma yammacin Afirka ne ke lallon tashar AREWA24 ta tauraron dan dan’adam na Eutelsat kyauta, haka kuma, a Najeriya ana kallon tashar akan StarTimes da ake biya (tasha mai lamba 138), da kuma kafar tauraron dan’adam ta StarTimes DTH (tasha mai lamba 538) sannan da kafafen tauraron dan’adam na kamfanin Multichoice guda biyu da ake biya, wato DSTV (tasha mai lamba 261) da kuma Gotv (tasha mai lamba 101).
Haka kuma ana dora ingantattun shirye-shiryen tashar AREWA24 kowanne mako a shafin youtube.com/AREWA24channel, sannan tashar na amfana da masu kasancewa da ita a shafukanta na AREWA24.com, da facebook.com/AREWA24, da Instagram.com/AREWA24channel, da kuma na twitter.com/AREWA24channel. Domin karin bayani sai ku tuntubi: info@arewa24.com
Post Views: 10,712